Kodinatan NNPP na Arewa maso Gabas da Magoya Bayan Kwankwaso Sun fice daga Jam’iyyar zuwa PDP

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria
 Kasa da mako guda da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso ya ziyarci jihar Bauchi, kodinetan jam’iyyar na shiyyar Arewa maso Gabas, Dr Babayo Liman da daruruwan magoya bayansa sun fice daga NNPP zuwa jam’iyyar PDP a jihar.
 Da suke ganawa da manema labarai a sakatariyar kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ), a Bauchi, sun bayyana goyon bayansu ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar.
Talla
 Liman ya ce Atiku Abubakar ya na da kwarewa da gogewar da zai ceto kasar nan daga halin kunci da tabarbarewar tattalin arzikin da take ciki idan aka yi la’akari da abubuwan da ya yi a baya a matsayinsa na tsohon mataimakin shugaban kasa na tsawon shekaru takwas.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
 Ya ce, “Na zo nan ne domin in sanar da manema labarai da sauran jama’a cewa a yau ni Babayo Liman na yi murabus daga mukamina na sakataren shiyya na NNPP kuma dan kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, sannan ko’odineta na Kwankwasiyya, na fice daga jam’iyyar na koma jam’iyyar PDP.
 “Anan ina tare da wasu shugabannin zartarwa na NNPP da dubban magoya bayana domin bayyana aniyar mu ta komawa jam’iyyar PDP da kuma goyon bayan takarar Alhaji Atiku Abubakar a matsayin shugaban Najeriya da Bala Mohammed a matsayin gwamnan jihar Bauchi .
 “Ina kira ga dukkan magoya bayana a yankin Arewa maso Gabas da su bi matakina na ficewa daga jam’iyyar NNPP zuwa PDP, sannan kuma ina kira ga magoya bayana a jihar Bauchi da su yi hakan don ceto kasata Nigeria.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...