Bana Jin dadin yadda wasu suke kirana da Jibrin dan Sudan – Buhari

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

 

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce iƙirarin da wasu ke yaɗawa cewa wani mutum ne mai suna Jubril daga Sudan yake mulkin Najeriya ba abin dariya ba ne kuma an ƙirƙire shi ne don kawar da hankalin gwamnatinsa.

 

Buhari ya bayyana haka ne cikin wani fim kan rayuwarsa da aka haska yayin bikin cikarsa shekara 80 da haihuwa na musamman da aka yi a Abuja.

 

Talla

Shugaban na mayar da martani ne ga wani shaci-faɗin da aka fara yaɗawa daf da ƙarewar wa’adinsa na farko a kan mulki cewa ya rasu amma wani mutum mai suna Jubril daga Sudan ne ya maye gurbinsa a Fadar Shugaban Ƙasa Aso Rock.

 

Ya ce masu ta da zaune tsaye ne suka ƙirƙiri maganar “saboda wulaƙanci”.

 

A cewarsa: “A’a, ba abin dariya ba ne saboda waɗanda suka ƙirƙiri zancen sun yi ne saboda wulaƙanci. Suna so su karkatar da hankalin gwamnati daga kan muhimman abubuwa.

 

“Babbar manufarmu ita ce yin ayyukan raya ƙasa, mu fargar da mutane su san cewa akwai buƙatar su yi aiki tuƙuru don su rayu cikin walwala.

 

“Suna [masu yaɗa iƙirarin] son su ji daɗin rayuwa ne kawai da kuma samun goyon bayan al’ummarsu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...