Rundunar sojin Sama ta kashe ƙasurguman ƴan fashin daji da ke addabar jihar Zamfara

Date:

Daga Daga Maryam Ibrahim zawaciki

 

 

Rundunar sojojin sama ta Najeriya tace jami’anta sun samu nasarar hallaka wasu ƙasurguman ƴan fashin daji waɗanda ke addabar ƙauyukan jihar Zamfara.

 

Rahoton Jaridar PRNigeria ya nuna cewa an samu nasarar kashe ƴan fashin ne a wasu hare-hare da jiragen sojojin Najeriya suka kai a wasu ƙauyukan jihar Kaduna.

 

Waɗanda aka kashen a cewar rahoton sun haɗa da Jibrin Gurgu, da Isah Jauro da kuma wani da ake kira Tambuwal.

 

Talla

Sauran sun haɗa da Noti, da Bala, da Yunusa da kuma Burti.

 

Bayanin da jaridar ta samo ya ce an kai farmakin ne a wasu sabbin sansanonin ƴan fashin a yankin ƙaramar hukumar Giwa da ke jihar Kaduna.

 

Haka nan an kai wasu hare-haren a yankunan ƙananan hukumomin Igabi da Birnin Gwari.

 

Wata majiyar tsaro ta ce an ga dacewar kai harin ne bayan rahotannin da ke cewa an samu ƙaruwar ayyukan ƴan bindiga a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...