Yan adaidaita sahu: Gwamnatin Kano ta magantu kan wahalar da mutan kano suka sha

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Mataimakin gwamnan jihar kano Dr Nasiru Yusuf Gawuna yace nan da jimawa kadan zata zauna domin sake yin duba kan sabuwar dokar hana yan adaidaita sahu bin wasu manyan tituna a Kano .

 

Talla

Mun sami labarin halin da al’umma suka shiga sakamakon Wannan doka, yanzu haka gwamnati ta bada dama a sake duba dokar don samar da abun da bazai musgunawa al’umma ba”. 

 

Mataimakin gwaman ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin ranar larabar nan.

 

Yace gwamnati ta tura jami’ai domin duba halin da al’umma suka shiga, Kuma ta ji koke -koken al’umma, zata ɗauki matakan saukakawa al’umma tunda dama gwamnatin ta al’umma ce .

 

” Duk abun da ya kamata a yi in Allah ya so nan da zuwa an jima kadan gwamnati ta sahale mu zauna mu duba mu gani, domin a kawo masalahar Wannan al’amarin, Kuma Ina tabbatarwa al’umma cewa bi’izinin lahi za’a yi abun da al’umma zasu ji dadin sa”. Inji Gawuna 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...