Daga Aisha Aliyu Umar
Kungiyar Izalatul bidi’a wa’ikamatussunah ta kasa ta bayyana matsayarta kan wanda zai Shugabanci Nigeria a kakar zaben shekara ta 2023 dake tafe.
Gwamnatin tarayya ta amince da Hutun haihuwa ga maza ma’aikata
“Muna addu’ar cikin yan takarar shugaban kasa tsakani Alhaji Atiku Abubakar Mai girma Wazirin Adamawa da Bola Ahmad Tinubu da Mai girma Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso wadanda duk Musulmi ne Muna rokon Allah ya zaba mana wanda zai zama alkhairi ga Nigeria da Musulunci”. Inji Kabiru Gombe

Sakataren kungiyar Sheikh Muhammad Kabiru Gombe cikin wata sanarwa da ya wallafa a sahihin shafinsa na Facebook yace Shugaban kungiyar na kasa ya bashi Umarnin su cigaba da yin addu’o’i Allah ya zabawa Nigeria da addinin musulunci wanda zai zama alkhairi gare su.
Yanzu-Yanzu: Gwamnatin jihar Kano ta haramta wa Yan Adaidaita Sahun bin Wasu Manyan Titunan Kano
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a zabuka mabanbanta kungiyar ta kan fadi Inda zata kar ka ta, Amma a wannan karon kungiyar ta ce addu’o’in kawai zasu yi domin duk manyan yan takarar Musulmi ne don haka baza su zabi wani su bar wani ba.