Rarara ya bayyana abun dake tsakanin su da Aisha Humaira

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Aisha Humaira dai tana daya daga cikin jarumai mata da tauraruwarsu ke haskawa A masana’antar kannywood, Sai dai anga kokaci guda ta jingine harkar fina-finan ta koma karkashin Kamfanin Mawakin wato Dauda Kahutu Rarara.

 

Kafin komawarta karkashin Kamfanin Na Mawakin, A Baya Ana Yawan Ganinta da mai shirya fina-finan nan Abubakar Bashir Mai Shadda, Inda bayan auren na mai shadda Kwatsam sai akaga ta koma wajen mawaki Rarara.

Talla

Hakan tasa mutane suka fara zargin c kamar akwai soyayya mai karfi a tsakaninsu da Rarara sakamakon yanda a koda yaushe ake ganin su tare, hakan tasa mutane da dama suke .

 

Sai dai a wata hira da akai da mawaki Rarara an tambaye shi :

Rarara da Humaira

“Shin Akwai Soyayya Ne TsakaninKa Da Jaruma Aisha Humaira?”

 

Mawaki Rarara yace shi da Aisha Humaira ba soyayya bace kawai akwai kyakyawar alakar ta aiki a tsakaninsu, amma yace ba laifi bane kowa ya fadi abun da yake tunani.

” Aisha Humaira Darakta ce a kamfani na Kuma ita ce ta uku a kamfanin don haka dole a rika ganinmu tare da ita, kuma in ma da soyayya a tsakaninmu nan gaba ai zata fito tunda ita soyayya ai bata buya”. Inji Rarara 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...