IPMAN tace tallafin man fetur ba mai ɗore wa ba ne a kasar nan

Date:

 

 

Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta ƙasa (lPMAN), ta ce tallafin da ake biya a kan man fetur ba dawamamme ba ne.

 

Mike Osatuyi, Kwanturolan ayyuka na kasa na lPMAN, a wata hira da kamfanin dillancin labarai na ƙasa (NAN) a yau Litinin a Legas, ya yi Allah wadai da biyan tallafin man fetur.

 

Osatuyi ya bayyana hakan ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun karin farashin man fetur a gidajen mai a fadin kasar nan.

Talla

Ya ce gwamnatin tarayya ta kashe Naira tiriliyan 20.51 a kasafin kudin shekarar 2023 a kan kudaden shiga na Naira tiriliyan 9.7, inda ya bar gibin Naira tiriliyan 10.78.

 

Osatuyi ya ce gwamnati na fatan bayar da tallafin man fetur har zuwa watan Yunin 2023 kan kudi Naira tiriliyan 3.6, a kan N435 na farashin dala na babban bankin Najeriya (CBN).

 

“A halin yanzu, farashin a hukumance na CBN ya kai kusan N445 zuwa dala daya wanda ya haura N435 zuwa dala da aka ƙiyasta a kasafin kudin shekarar 2023,” inji shi.

Ranar ciwon Suga: Yara da yawa na kamuwa da cutar a Nigeria -Masana

Ya ce tsarin bayar da tallafin ya haifar da ƙaruwar giɓin kasafin kuɗi tare da haifar da koma baya ga rancen tattalin arziki.

 

Ya kuma ce tallafin ya sa fasa-kwaurin man fetur ya zama sana’a da a ke rububi saboda ribar da ake samu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...