Gobara ta hallaka mutane 3 tare da kone shaguna sama da 100 a kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Hukumar kashe gobara ta jihar kano ta tabbatar da konewa akalla shaguna sama da guda 100 a kasuwar yan tumatur dake Badume a Kano.

 

” A ranar Juma’a da misalin karfe 03:30 na yamma wani mutum mai suna Ibrahim tsalha ya kirawo ofishin mu ya sanar da mu tashin wata gobara a kasuwar Badume dake karamar hukumar Bichi, hakan tasa jami’an hukumar mu na Bichi suka taso domin kashe gobarar”.

 

Jami’in hulda da jama’a na na hukumar kashe gobara ta jihar kano PFS Saminu Yusuf Abdullahi ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da ya aikowa kadaura24.

Talla

Yace kafin isar jami’ansu wurin wutar ta kone shaguna sama da guda 100, tare Kuma da jikkata wasu mutane guda 3 maza biyu mace daya.

 

“Bayan mun fito da mutanen cikin mummuna yanayi daga bisa ni dukkanin sun rasu Kuma mun mika kawawwakin ga wani jami’in Rundunar yan sanda dake ofishin yan sanda na Bichi wato Isfecta Mukaila Inuwa” . Inji Saminu Yusuf

Sanarwar ta Kara da cewa kashe wutar ta tseratar da akalla shuguna 100, sannan Kuma har yanzu ana bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin.

Ya yi kira ga al’ummar jihar kano baki daya dasu rika kashe wutar lantarki tare da cire duk wani abun wuta daga jikinta a duk lokacin da suka gama amfani da ita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...