2023: Akwai kyakyawan yakinin Kwankwaso zai janyewa Tinubu takara Shugaban kasa – Musa Iliyasu

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Dan takarar majalisar tarayya a kananan Hukumomin kura madobi da garun Mallam a jam’iyyar APC Hon. (Dr) Musa Iliyasu Kwankwaso yayi Zargin cewa akwai kyakyawan yakinin Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso zai janye daga takarar shugaban kasa da yake yi jam’iyyar NNPP ya kuma marawa dan takarar APC Asiwaju Bola Ahmad Tinubu.

 

Musa Iliyasu Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da masu ruwa da tsaki na Jam’iyyar APC a karamar hukumar kura, a kokarin sa na tunkarar zabukan shekara ta 2023.

 

Yace alamu na cigaba da nuna cewa Sanata Kwankwaso zai hakura da takarar sa ya marawa dan takarar shugaban kasa na APC baya , saboda abun da ya kirawo bazai iya yin takarar ba.

Talla

” Irin wannan abubuwan da na gano tun tuni shi sanata Malam Ibrahim Shekarau ya gani yasa ya fice daga jam’iyyar NNPP ya koma jam’iyyar PDP, Kuma Ina tabbatar muku idan zaben ya mazo zaku gani”. Musa Iliyasu Kwankwaso

 

Musa Iliyasu Kwankwaso yace rashin tabbacin yin takarar Kwankwaso da wasu matsaloli Masu yawa ne yasa kullam yan kwankwasiyya suke ficewa daga tsarin suke komawa jam’iyyar APC.

 

Talla

A yayin taron Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso ya karbi matasa maza da mata yan kwankwasiyya Yan social media wadanda suka ce sun ajiye tafiyar kwankwasiyya sun rungumi tafiyar jam’iyyar APC.

 

Zainab Husaini madobi ita ce ta yi magana a madadin matasan da yawansu ya haura 30, ta ce zasu bada duk gudunmawar da ake bukata domin ganin Musa Iliyasu Kwankwaso da sauran yan takarar APC sun yi nasara a zaben shekara ta 2023.

 

Kwankwaso dai shi ne jagora Kuma Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a zabukan shekara ta 2023 dake tafem

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...