Hirar da Safara’u ta kwana 90 ta yi da BBC ta janyo cheche-kuche

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Hirar da tsohowar jarumar fim din kwana chasa’in na Arewa24 Safara’u wacce bayan ta fara waka ta koma Saffa ta yi da sashin Hausa na BBC ta janyo cheche-kuche a tsakanin mata musamman a kafafen sada zumunta na social media.

A jiya litinin a Hirar da tayi da BBC Hausa saffa bayan an tambaye ta yadda ta ji game da fitar bidiyon tsaraicinta , sai ta ce ta damu sosai Inda har sai da ta kai ko wajen bata fita saboda gudun tsangwamar da Zata fiskanta.

Wasu Magoya bayan Shekarau da suka shiga NNPP tare sun jaddada goyon bayan su ga Kwankwaso

Babban abun da ya jawo cheche-kuchen shi ne da tace “kowacce mace tana yin hoto ko bidiyon tsaraicinta ta bar shi a wayarta saboda da nishadi”.

 

Safara’u a cikin shirin kwana chasa’in

 

Wannan kalamai basu yiwa mata da yawa a shafukan sada zumunta dadi ba, hakan tasa suke ta mayar mata da martani wasunsu ma har da zagi saboda abun da suka kirawo bata musu suna da ta yi.

Baya ga mata maza ma sun shiga cikin Masu yin Allah Wadai da Wadancan kalamai na jaruma Safara’u wacce yanzu aka fi saninta da suna Saffa.

Dama dai Safiyar Yusuf wato saffa tana shan suka kan yadda take gudanar da harkokin wakokinta cikin Rashin bin tsarin al’adun Hausawa da Kuma sabawa addinin musulunci ta hanyar kalamai da Kuma shigar da take yi.

Yanzu-Yanzu : Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu sakamakon ruftowar wani gini a kasuwar Beruet dake kano

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito Hukumar tace fina-fina ta jihar kano ta aiyana Neman mawakiyar saboda korafe-korafen da hukumar ta karba daga al’ummar jihar kano na rashin mutunta al’adun mutane kano a cikin wakokin Saffa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...