NIMET ta yi hasashen samun ruwan sama mai karfi a jihohi 5 na arewacin Najeriya

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya NIMET ta yi hasashen fuskantar kakkarfan ruwan sama na tsawon kwanaki 4 babu kakkautawa a wasu jihohin arewacin kasar 5 da kuma birnin Abuja fadar gwamnatin kasar.

 

Cikin rahoton hasashen yanayin da hukumar ta NIMET ta fitar ta ce jihohin da za su fuskanci wannan ruwa na tsawon kwanaki 4 ba tare da kakkautawa ba sun kunshi Kaduna da Neja da Bauchi da Pulato da kuma jihar Nassarawa baya ga birnin Tarayyar kasar.

 

Rahoton na NIMET ya kuma yi hasashen fuskantar madaidaicin ruwan sama a wasu jihohin Najeriya daga kudanci da arewaci da suka kunshi, Kwara da Oyo da Kogi da Ekiti da Ondo baya da Sokoto da Katsina da Zamfara.

Ambaliyar ruwa: Gwamnatin Kano za ta rushe gine-gine da a ka yi kan hanyoyin ruwa

 

Sauran jihohin da za su fuskanci mamakon ruwan sun hada da Kebbi da Kano da Jigawa da Yobe Borno da Gombe da Adamawa da Taraba da Benue da Cross River da Akwa Ibom kana Ebonyi da Enugu da Abia da Imo da Anambra da Rivers da Edo da kuma jihar Delta.

 

Hukumar ta NIMET ta bukaci daukar matakan gaggawa don kaucewa fuskantar ambaliya musamman la’akari da cewa dukkanin jihohin da ta lissafa kama daga wadanda za su fuskanci mamakon ruwan da wadanda za su fuskanci madaidaici da kuma kakkarfa, kowannensu zai zo da kakkarfar iska.

Akwai yiwuwar gwamnatin tarayya zata ciyo bashin Naira Tiriliyan 11a shekara ta 2023 – Ministar Kudi

 

Wannan rahoto na zuwa ne a dai dai lokacin da ambaliyar ruwa a jiya litinin ta kashe mutane 3 tare da raba iyalai 495 da muhallansu.

 

Masana dai na ci gaba da gargadin jama’a kan muhimmancin yashe magudanan ruwa da kuma kaucewa tuki a cikin ruwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...