Gwamnatin Kogi ta rufe gidajen karuwai, ta kuma hana sanya takunkumi

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Gwamnan Jihar Kogi da ke tsakiyar Najeriya, Yahaya Bello, ya bayar da umarnin rufe gidajen karuwai a fadin jihar.

 

Kazalika ya haramta sanya takunkumai a bainar jama’a da zummar ganin cikakkiyar fuskar kowa domin magance matsalar tsaro.

 

Wannan umarni ya biyo bayan matsalolin tsaro da ake samu a wasu sassan jihar.

 

Talla

Gwamna Bello ya bayar da umarni ne ranar Talata a Lokoja yayin taro da sarakunan gargajiya na jhar.

 

Gwamnan ya bayar da umarnin rusa yankunan da ake kama-wuri-zauna da ke Lokoja, Osara, Zango, Itobe, Obajana, da wasu sassan jihar.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...