Ana zargin ‘yan Vigilante da kashe malamin makarantar allo a Jihar Kano

Date:

Daga Umar Ibrahim

 

Ana zargin ‘yan kungiyar sintiri (vigilante) da kashe wani malamin makarantar allo a unguwar Dabai, da ke karamar hukumar Gwale a Jihar Kano.

 

Shi dai Musa Mai-Almajirai, sanannen malamin Qur’ani ne a unguwar, inda yake da daruruwan almajirai.

 

Ana zargin ‘yan kungiyar sintirin da yi wa malamin dukan tsiya a ofishinsu bayan da aka kai shi can bisa zargin da wata mata ta yi masa na yunkurin satar yaro.

Talla

Jaridar Premium Times ta intanet ta ruwaito cewa dan malamin, Ibrahim ya sheda mata cewa, ”Mahaifin nasa yana tafiya ne sai ya ji kukan jariri sabuwar haihuwa a wata bola.

Da dumi-dumi: Gwamna Ganduje da Sarki Sanusi sun yi kicibis a Abuja

Sai ya je ya dauki yaron, sai kawai wata mata ta yi masa ihu, tana ce masa barawon yaro.”

 

”Kururuwar da matar ta yi ce ta janyo ‘yan kungiyar sintirin da sauran jama’ar unguwar wadanda suka rufe shi da duka,” in ji dan.

NDLEA ta rufe gidan abincin da take zargin ana sayar da kayan maye a Kano

 

Ya kara da cewa, ”Daga nan sai suka tafi da shi ofishinsu suka ci gaba da dukansa. Daga baya ya fadi ya suma.”

 

Ya ce,” Bayan da wasu ‘yan unguwar suka gane shi sai suka garzaya da shi asibiti, inda ya cika a hanya.”

 

Dan malamin ya sheda wa jaridar cewa ‘yan-sanda sun kama shugaban ‘yan-sintirin na unguwar, mai suna Munkaila, inda ake bincikensa a caji ofis na Rijiyar Zaki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...