Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso ya mika ta’aziyyar rasuwar Dogarinsa

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

 

Shugaban karamar hukumar kumbotso, Alhaji Hassan Garba Farawa ya mika sakon ta’aziyya ga babban sufeton ‘yan sandan kasar nan, kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano da daukacin jami’an tsaro da ke aiki a yankin bisa rasuwar ADC Junaidu Ayuba. wanda ya rasu bayan fama da matsalar koda na tsawon lokaci.

 

Shugaban wanda ya nuna alhininsa bisa ga rasuwar Dogarin nasa, sannan mika sakon ta’aziyyar ga iyalai da yan uwan mamacin.

 

Cikin wata sanarwa da hadimin shugaban karamar hukumar kan harkokin yada labarai Shazali Saleh farawa ya aikowa kadaura24 yace Rasuwar ta zo ne sa’o’i 24 bayan da shugaban ya tafi kasar Saudiyya don gudanar da aikin hajjin shekarar 2022.

 

A cikin sakon juyayi ga hedikwatar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kano, da iyalan marigayi Junaidu, Garba Farawa ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ba ga iyalansa kadai ba har ma da mutanen kumbotso baki daya.

 

Yana mai addu’ar Allah s.w.t ya gafarta masa zunubansa, yasa Aljannatul Firdausi ce makomarsa.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...