Buhari Zai Rantsar Da Mai Shari’a Ariwoola A Matsayin Alkalin Alkalai na kasa

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

A yau Litinin ne ake sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai rantsar da mai shari’a Olukayode Ariwoola a matsayin mukaddashin alkalin alkalan Najeriya (CJN).

 

 

Hakan ya biyo bayan murabus din mai shari’a Ibrahim Tanko Muhammad bisa dalilan lafiya.

 

Mai shari’a Ariwoola, wanda shi ne babban alkalin kotun koli, za a rantsar da shi da misalin karfe biyu na rana a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

 

Majiyoyi sun ce zai yi aiki a matsayin alkalin alkalai har zuwa lokacin da shugaban kasa zai mika sunansa ga majalisar dattawa domin tabbatar da shi a matsayin babban alkalin alkalan Najeriya (CJN).

 

An haife shi a ranar 22 ga watan Agustan 1954, Mai shari’a Ariwoola dan jihar Oyo ne, ya taba zama mai shari’a na kotun daukaka kara kafin daga bisani a daukaka shi zuwa kotun koli a shekarar 2011.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...