An fara shari’ar wasu yan fashi da suka so su yi garkuwa da wani yaro a Kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Wasu mutane da ake zargi da fashi da makami sun yi barazanar tafiya da dan wani mutum da sukaje gidansa domin fashi shi kuma yai musu turjiya.

An gurfanar dasu a gaban kotun Majistare Mai Lanba 58 karkashin jagorancin Aminu gabari, inda ake tuhumarsu da hada kai da fashi da makami da yunkuurin aikata kisan kai da Samar da mummunan Rauni.

A zaman kotun Lauyan gwamnati Kuma Mai gabatar da Kara Sadik Isa Fara, ya bukaci a karantowa wadanda ake tuhuma laifinsu inda Jamiin kotu Habibu Abdurrahman (Dan boy ) ya karanto musu kunshin tuhumar.

Tunda fari dai Ana zargin Nazir Abdullahi da Tijjani Garba da Aminu Abdullahi da kuma Salisu Abubakar da zuwa unguwar Tudun Fulani suka dinga shiga gida-gida suna yiwa mutane fashi a gidajansu, daga cikin wadanda suka yiwa fashin harda Wanda sukayi garkuwa da dansa dan shekara biyu lokacin da yaki amincewa da bukatarsu haka Kuma Ana zargin sun datsewa wani mutum hannu da adda.

Wakiliyar kadaura 24 Rukayya Abdullahi Maida ta rawaito mana cewa, bayan karanta musu kunshin tuhume- tuhumen sun musanta zagin Wanda daga Nan Kuma kotun ta aike dasu zuwa gidan gyaran Hali har zuwa ranar 27/7/2022 domin sake gabatar dasu don cigaba da shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...