Har Yanzu Buhari bai bayyana Wanda yake goyon baya ba – Fadar Shugaban kasa

Date:

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta labarin da ke cewa shugaba Muhammad Buhari ya goyi bayan guda daga cikin masu neman takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC.

Mai magana da yawun shugaban, Malam Garba Shehu ya bayyana haka a yau lahadi a wata sanarwar da ya fitar.

Ya ce sam–sam shugaban bashi da wani da ya ke so a matsayin dan takarar sa la’kari da yawan mutanen da suka nemi yiwa APC takarar shugabancin kasa a zaben na 2023.

Ya kara da cewa ba demokradiyya ba ce Buhari ya zabi mutum guda shi ka dai a matsayin wanda zai yi wa Jam’iyyar takara.

Sai dai ya ce shugaban na goyon bayan yin masalaha ne kasan cewar yin hakan ka’iya saukaka zaben cikin gida da Jam’iyyar ke shirin gudanarwa a makonnan da muke ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...