Bunkasa noma: Alhassan Ado ya sayi gonaki don fadada Kamfanin Shinkafa dake T/wada

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam

A kokarin sa na cigaba da ingantawa da samar da Sana’o’i ga matasa da maza Mata Shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai natarayyar Rt Hon Alhassan Ado Doguwa sardaunan Rano ya sake sayen wasu gonaki domin fadada kamfanin sarrafa shinkafa dake yankin karamar hukumar Tudun wada.

Cikin Wata sanarwa da Mataimaki na musamman ga Shugaban Majalisar wakilai Auwal Ali Sufi ya aikowa Kadaura24 yace Hon Alhassan Ado Doguwa ya biya kudi kimanin Naira miliyan biyu da dubu dari takwas domin bunkasa Wannan masana’anta, wadda itace ta farko a tarhin yankin.

Rahotanni sun nuna babu wani Dan majalisar Tarayya da yayi irin Wannan aikin na kafa kamfanin sarrafa shinkafa a duk fadi jihar kano in ba Sardaunan Rano ba

Shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai tar Rt Hon Alhassan Ado Doguwa yayi nazari wajen kawo Wannan aikin Alheri domin kakkabe Zaman kashe wando a tsakanin matasa dake yankin kano ta kudu baki Daya dama bunkasa harkokin noma a yankin.

Tuni Dai aka biya kudi kimanin Naira miliyan biyu da dubu dari 8 ga masu gonakin da suka amince suka sayar, domin aiki Zai ciyar da al’ummar Kananan Hukumomin Doguwa da Tudun Wada cigaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...

Shaye-shayen kwayoyi: Al’ummar Unguwar Rimin Kebe sun nemi agajin mahukunta

Daga Ibrahim Sani Gama   Kungiyar cigaban matasan unguwar Rimin Kebe...

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...