Bunkasa noma: Alhassan Ado ya sayi gonaki don fadada Kamfanin Shinkafa dake T/wada

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam

A kokarin sa na cigaba da ingantawa da samar da Sana’o’i ga matasa da maza Mata Shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai natarayyar Rt Hon Alhassan Ado Doguwa sardaunan Rano ya sake sayen wasu gonaki domin fadada kamfanin sarrafa shinkafa dake yankin karamar hukumar Tudun wada.

Cikin Wata sanarwa da Mataimaki na musamman ga Shugaban Majalisar wakilai Auwal Ali Sufi ya aikowa Kadaura24 yace Hon Alhassan Ado Doguwa ya biya kudi kimanin Naira miliyan biyu da dubu dari takwas domin bunkasa Wannan masana’anta, wadda itace ta farko a tarhin yankin.

Rahotanni sun nuna babu wani Dan majalisar Tarayya da yayi irin Wannan aikin na kafa kamfanin sarrafa shinkafa a duk fadi jihar kano in ba Sardaunan Rano ba

Shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai tar Rt Hon Alhassan Ado Doguwa yayi nazari wajen kawo Wannan aikin Alheri domin kakkabe Zaman kashe wando a tsakanin matasa dake yankin kano ta kudu baki Daya dama bunkasa harkokin noma a yankin.

Tuni Dai aka biya kudi kimanin Naira miliyan biyu da dubu dari 8 ga masu gonakin da suka amince suka sayar, domin aiki Zai ciyar da al’ummar Kananan Hukumomin Doguwa da Tudun Wada cigaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...