Bamu da masaniyar batun kitsa tsige shugabannin majalisar dokokin Kano – Labaran Abdul Madari

Date:

Daga Sajida Ahmad

Majalisar dokokin jihar Kano ta musanta raɗe-raɗin da ake yaɗawa ta fara yunƙurin tsige shugaban majalisar Rt Hon Hamisu Ibrahim Chidari da mataimakin sa Hon Hamza Massu.

Shugaban masu rinjaye na Majalisar Hon. Labaran Abdul Madari ne ya bayyana hakan Yayin wata ganawa da yayi da gidan Radio Aminchi dake kano.

Madari yace basu da masaniyar wani yunkuri na tsige Shugaban Majalisar,Kuma yace labarin ba shi da tushe ballantana makama.

“Mun yanzu Muna Abuja ma dukkanin mu har da Shugaban Majalisar Rt. Hon. Hamisu Ibrahim chidari Inda Muka zo Rantsar da Shugaban jam’iyyar APC na Jihar kano Abdullahi Abbas Dan sarki jikan Sarki”. Inji Madari

Shugaban Majalisar yace Suna da kyakykyawar mahimta a tsakanin su Kuma yace bai ma ga dalilin da zai sa a tsige Shugaban Majalisar ba.

Wasu rahotanni sun nuna dai sun zargi cewa Kwamishinan ƙananan hukumomi Murtala Sule Garo ne ya kitsa tsige shugabannin, inda ya baiwa shugaban masu rinjaye na majalisar Hon Labaran Abdul Madari umarnin gudanar da shirin.

Shugaban masu rinjaye na majalisar yace babu ƙamshin gaskiya ko kadan akan Zargin.

Ku saurari hirar mu dashi 👇

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...