Mahaifiyar Limamin Masallacin Al-Furqan, Dakta Bashir Aliyu ta rasu

Date:

 

Mahaifiyar fitaccen Malamin addinin musuluncin nan na Jihar Kano, Dakta Bashir Aliyu Umar ta rasu.

Marigayiyar, mai suna Hajiya Khadija Aliyu Harazumi ta rasu da safiyar yau Talata a gidanta da ke Gwale Gudundi bayan ta yi rashin lafiya.

Hajiya Kahdija daya ce daga cikin matan Dan Amar Kano Alhaji Aliyu Harazumi Umar.

Ta rasu ta bar ƴaƴa da jikoki da dama.

Daga ciki akwai babban limamin masallacin juma’a na Al-Furqan da ke unguwar Nasarawa a birnin Kano Dr Bashir Aliyu Umar

Haka kuma za a yi jana’izarta a Kofar Kudu da ke gidan Sarkin Kano da misalin ƙarfe 3 na yamma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta...

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...