Zargin Rashawa: Kotu ta kori karar da aka zargi Gen. Idris Danbazau da karbar na goro

Date:

Babbar kotun Jihar Kano Mai lamba 14 ta kori karar da wani Dan kasuwa Mai Suna Sani Isma’ila ya shigar gabanta yana zargin Shugaban Hukumar Kare hakkin Mai saye da mai sayarwa Janar Idris Bello Danbazau Mai ritaya ya nemi na Goro a Wajensa tare Kuma da Zargin Jami’an Hukumar sun kama masa kayansa ba bisa ka’ida ba.

Alkalin Kotun Mai Shari’a Nasiru Saminu ya yi watsi da karar, Inda yace akwai Hukumar da take da alhakin bincike Kan harkokin da suka shafi cin hanci da rashawa.

Kotun ta Kuma bada Umarnin a Cigaba da ajiye Kayan Mai Kara Wanda dama man ja yake sayarwa a Kasuwar Galadima , Kuma dama Hukumar tace ta maka man ne saboda gurbataccene ake sayarwa al’umma.

Kadaura24 ta rawaito Barr. Abubakar Salisu Muhd shi ne lauyan Hukumar Mai saye da mai yace sun gamsu da yadda Shari’ar, Inda yace an kori Shari’ar ne Saboda rashin hujjojin da suka gabatar a gaban Shari’a.

Yace za a Cigaba da ajiye gurbataccen Man Jan har Lokaci da Hukumar dake da alhakin binciken karbar zargin na goron .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...