Kotu ta yanke wa wani kurma hukunci sakamakon sayar da wiwi a Kano

Date:

 

Kotun Majistare mai lamba 47, ƙarƙashin Mai Shari’a Hadiza Muhammad Hassan, a jiya Litinin ta yanke wa wani kurma hukunci har kashi uku.

Tun da fari dai, an gurfanar da kurman ne bisa tuhumar haɗa kai da uzzurawa al’umma wajen haɗin gwiwa da wasu ɓatagari su na siyar da tabar wiwi.

Ko da jami’in kotun, Auwal Yakubu Abdullahi ya karanto masa tuhumar, nan take ya amsa laifin sa, inda hakan ya sa kotu ta yanke masa wannan hukuncin.

Daily Nigerian ta rawaito Hukuncin farko, an yanke masa wata 6 ko tarar naira dubu 10, sai kuma ɗaurin shekara 1 ko tarar naira dubu 30, sannan kuma sai ɗaurin wata uku ko tarar naira dubu 10.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...

Kungiyar Karamci United Family ta Karrama Shugaban gidan Radiyon Pyramid Saboda Taimakawa Al’umma

Shugaban gidan Radio tarayya Pyramid FM Dr. Garba Ubale...

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...