Wanda ake zargi da kisan Hanifa Abubakar ya ce bashi ya kwashe ta ba

Date:

A zaman kotun na yau Litinin karkashin  mai shari’a Usman Na’abba, Abdulmalik Tanko ya ce kokadan ba shi ya kashe Hanifa Abubakar ba kuma bashi da masaniya kan aikata kisan.

Kadaura24 ta rawaito bayan da aka gurfanar da shi a gaban babbar kotun jiha ranar litinin wanda ake zargin ya ce ya yarda ya sace ta amma bashi ya kashe ta ba.

Idan za a iya tunawa dai a baya Abdulmalik Cikin Wani faifen video da Jami’in hulda da Jama’a na yan sandan Jihar Kano ya wallafa a Shafin Facebook, ya amsa kisan Hanifa bayan da rundunar ‘yan sanda ta yi holinsa a shalkwatarsu.

Har ma ya bayyana cewar ya kasheta ne da shinkafar bera ta N100 bayan da ya saceta ya kuma boyeta a wani wuri.

Wannan ce ta sanya alkalin kotun ya dage shari’ar har zuwa ranar 2 da 3 ga Maris mai kamawa domin sauraron karar, ya kuma bayar da umarnin a ci gaba da tsareshi a gidan yari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...