KSADP ya kudirci Inganta Rayuwar Mata ta hanyar Samar da Cibiyar tattara Nono

Date:

Daga Nazifa Ahmad Sagagi
 Shirin gina cibiyoyin tattara madarar madara guda 200 a jihar Kano da Shirin bunkasa noma da kiwo na jihar Kano, KSADP, sun kudirci aniyar inganta bangaren samar da Madarar shanu da nufin  inganta rayuwa da makiyaya musamman mata.
 Sanarwar da Shugaban yada labaran Shirin Ameen K Yassar Shugaban Shirin na KSADP, Malam Ibrahim Garba Muhammad ne ya bayyana haka a lokacin bude taron masu ruwa da tsaki kan cibiyoyin tattara madara, a Kano, inda ya bayyana cewa bankin ci gaban Musulunci da Asusun Raya al’umma LLF ne suka dauki nauyin aikin.
 “Wannan wani muhimmin mataki ne na bunkasa harkokin madara wanda zai inganta Rayuwar makiyaya musamman mata, ta hanyar tabbatar da ingancin madara, tsafta da Kuma ribarta”.
 “Da wannan ci gaban, wanda kuma zai haifar da alaƙa da Mata Masu sayar da nono da manyan ƴan wasa a harkar tattara madara da Kasuwancin ta, zai taimaka wajen rage wa Matan karkara wahalhalun da suke fuskanta na tafiyar Kasa da sayar da nono ba a farashi Mai rahusa”. Inji sanarwar
 Ya ce idan aka inganta hanyoyin tattara madara da adanata da kuma Kasuwancin ta, makiyaya da gwamnati za su samar da ingantaa hanyar shiga da kuma taimakawa wajen dakile kashe kudaden da gwamnatin tarayya ke kashewa wajen shigo da madara daga kasashen waje.
 Malam Ibrahim ya bayyana cewa daga cikin cibiyoyin tattara madara guda 200 da KSADP za ta gina, za a gina 40 tare da samar da kayan aiki a fadin kananan hukumomi 15 na jihar a bana.
 Hajiya A’isha Muhammad Abubakar, shugabar mata ta MACBAN ta kasa, ta bukaci mata da su taka muhimmiyar rawa wajen tafiyar da harkokin MCC saboda irin rawar da ake takawa a harkar kiwo tun daga nono har zuwa kasuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...