Gwamnatin Najeriya ta gano masu daukar nauyin Boko Haram 96

Date:

 

Hukumar da ke tattara bayanan sirri kan kudade ta bankado masu samar da kudi dan ta’addamci 96 har da masu alaka da kamfanonin hada-hadar kudi 424.

Ministan yada lanarai da al’adu na Najeriya Lai Mohammed ne ya bayyana hakan ne a yau, yayin wani bayani da ya yi kan yaki da cin hanci da gwamnatin shugaba Buhari ke yi.

Ya kara da cewa an gano kamfanoni 123 da kamfanonin 33 na masu musayar kudi da ke da alaka da ‘yan ta’adda a Najeriya.

Ya ce, “A bangarenta, a sharhin da ta yi kan kudade na 2020-2021, ta bayyana masu hada-hadar kudade 96 da ke da alaka da ‘yan ta’adda a Najeriya, akwai kuma wasu 424 da ke samar da kudade domin ta’addanci da suka hadar da kamfanoni 123, da kuma na masu musayar kudi 33, bugu da kari an gano wasu 26 da ake zargi da ta’addanci da wasu 7 da ake hada kai da su kan harkokin ta’addanci. Wannan bayani ya kai ga kama 45 da ake zargi wadanda kwanan nan za a gabatar da su a gaban kotu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...