Gwamnatin Najeriya ta gano masu daukar nauyin Boko Haram 96

Date:

 

Hukumar da ke tattara bayanan sirri kan kudade ta bankado masu samar da kudi dan ta’addamci 96 har da masu alaka da kamfanonin hada-hadar kudi 424.

Ministan yada lanarai da al’adu na Najeriya Lai Mohammed ne ya bayyana hakan ne a yau, yayin wani bayani da ya yi kan yaki da cin hanci da gwamnatin shugaba Buhari ke yi.

Ya kara da cewa an gano kamfanoni 123 da kamfanonin 33 na masu musayar kudi da ke da alaka da ‘yan ta’adda a Najeriya.

Ya ce, “A bangarenta, a sharhin da ta yi kan kudade na 2020-2021, ta bayyana masu hada-hadar kudade 96 da ke da alaka da ‘yan ta’adda a Najeriya, akwai kuma wasu 424 da ke samar da kudade domin ta’addanci da suka hadar da kamfanoni 123, da kuma na masu musayar kudi 33, bugu da kari an gano wasu 26 da ake zargi da ta’addanci da wasu 7 da ake hada kai da su kan harkokin ta’addanci. Wannan bayani ya kai ga kama 45 da ake zargi wadanda kwanan nan za a gabatar da su a gaban kotu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...