Daga Rukayya Abdullahi Maida
Shugaban karamar hukumar Garko Alhaji Salisu Musa Sarina ya yabawa Gwamnatin jihar kano bisa aiyukan raya kasa da take aiwatarwa al’ummar jihar.
Kadaura24 ta rawaito Alhaji Salisu Sarina ya bayyana hakan ne yayin da kwamashinan Ma’aikatar raya karkara da cigaban al’umma na jihar Kano Alhaji Musa Iliyasu kwankwaso ya zayarci fadar hakimin yankin.
Shugaban karamar hukumar wanda daraktan Mulki na yankin Alhaji Halilu Kunya ya wakilta yace duba da tarin aiyukan da gwamnati mai ci yanzu ta ke gudanarwa a fadin jahar nan ya zama wajibi a yaba mata.
Da yake nasa jawabin kwamashinan Ma’aikatar raya karkara Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso yace sun ziyarci yankin ne don wayar da kan al’umma akan Shirin gwamnati na samar da hasken wuta mai amfani da hasken rana ga al’umma musamman mutanen karkara.
Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso wanda mai taimaka masa na musamman Alhaji Abdulhamid Yusuf ya wakilta yace shirin zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin al’ummar jihar nan, kuma shirin zai baiwa matasan yankin yadda ake gyaran kayayyakin na’ura mai amfani da hasken rana.
Anasa bangaren hakimin Garko Dandarman Gaya Alhaji Adamu Abdullahi Adamu wanda Alhaji Mamuda Abba ya wakilta ya godewa gwamnatin jiha bisa nuna damuwarta ga Jama’ar jihar nan a inda ya bayar da tabbacin goyan bayan da hadin kan iyayen kasa.
A wani cigaban kuma kwamashinan ya makamanciya ziyarar ga karamar hukumar Wudil mataimakin shugaban karamar hukumar Alhaji Labilu Ismail ya tarbeshi a cibiyar yada addinin yankin.
Alhaji Labilu Ismail ya bayyana aniyar karamar hukumar na marawa dukkan kyawawan tsare- tsaren gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje baya da ya kamata domin samun nasarar inganta rayuwar al’umma.
I got this site from my pal who told me regarding
this web site and now this time I am visiting this web site and reading very informative posts at
this place.