Twitter sun ce sun ji dadin dawo wa Nigeria

Date:

Dandalin sada zumunta na Twitter ya bayyana jin daɗinsa game da matakin gwamnatin Najeriya na dawo da ayyukan shafin a ƙasar bayan wata bakwai.

“Mun ji daɗi ganin cewa mutanen Najeriya na iya amfani da Twitter,” a cewar kamfanin.

“Muna matuƙar son yin aiki a Najeriya, inda ake amfani da Twitter don kasuwanci da sadar da al’adu da kuma tattaunawa,” in ji Twitter cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinnsa na dandalin ranar Alhamis.

A ranar Laraba ne wata sanarwa daga fadar gwamnati ta ce Shugaba Buhari ya amince a cire haramcin amfani da Twitter daga 12:00 na daren Laraba.

Gwamnati ta rufe shafin ne a watan Yunin 2021 bayan ya goge wani saƙo na Buhari kan ‘yan bindigar da ke tayar da hankali a yankin kudu maso gabashin ƙasar, tana mai zargin kamfanin da yaɗa labaran “raba kan ƙasa”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...