Daga Aminu Abba
Gamayyar ‘yan adaidaita Sahu a jihar kano sun janye yajin aikin da suka tsunduma tun ranar litinin din data gabata sakamakon wani zama da akai da bangarensu da na gwamnati karkashin jagorancin Shugaban Kungiyar lauyoyi ta kasa reshen jihar Kano Barr. Mahmoud Gadanya.
Kadaura24 ta rawaito Barr. Abba Hikima dai shi ne ya wakilci bangaren yan adaidaita Sahun,yayin da Shugaban hukumar karota Baffa babba Dan agundi ya wakilci gwamnatin jihar kano.
Yayin zaman an cimma matsaya kamar haka:
1. Za a rubutawa gwamnatin jihar kano takardar Neman ragin kudin sabunta rigistar na naira dubu 8.
2. Yan adaidaita Sahu za su dawo aiki a gobe alhamis.
3 . za a jira gwamnatin ta tsaida matsaya kafin ranar 18 ga wannna wata da za a sake zama.
4 . Yan adaidaita Sahu za su cigaba da biyan Naira 100 harajin kullum-kullum.
Wadannan dai Su ne abun da aka cimma yayin zaman da aka gudanar a yau a ofishin Kungiyar lauyoyi ta kasa reshen jihar Kano, kuma yayin zaman kowanne bangare ya aminta da duk abubuwan da aka cimma.
Hello there! This is my first comment here so I just wanted to
give a quick shout out and say I really enjoy reading through your blog posts.
Can you suggest any other blogs/websites/forums that cover
the same topics? Thank you!