Kungiyar Tagwaye ta Jihar Kano ta Zabi Sabbin Shugabannin t

Date:

Daga Zara Jamil Isa
Kungiyar Inuwar Tagwaye ta kasa reshen jihar Kano (Twins forum)
ta gudanar da zaben shugabaninta karo na farko domin sake fasalin shugabancin kungiyar don inganta harkokin ta.
Shugaban kwamitin gudanar da zaben Hassan Isah Muhd Gwale shi ne ya jagoranci zaɓen har ma ya bayyana cewa Engineer Hássan Ahamad Makari a Matsayin sabon Shugaban Kungiyar, sai Kuma Hassan Auwal Muhd Jack city ya zama mataimakin shugaba, An Zabi Hussaini Kabir minjibir a Matsayin sakataren Kungiyar.
Da yake Ganawa da Wakilin Kadaura24 Hassan Isa Gwale ya bukaci wadanda suka samu nasarar a zaben da su yi aiki tukuru domin ciyar da kungiyar gaba.
Ya kuma bukaci wadanda basu samu Nasara a zaben ba, da su marawa wadanda suka samu nasarar baya domin ciyar da kungiyar gaba.
An dai gudanar da zaben ne a makarantar gidan makama da ke nan jihar Kano, inda tagwaye mata da maza daga ƙananan hukumomi arba’in da hudu suka halarci zaben.
Sabbin Shugabannin dai ana sa ran zasu tafiyar da harkokin Kungiyar dai-dai da yadda kundin tsarin Mulkin Kungiyar ya gindawa ba tare da son rai ba.
A Jawabinsa bayan rantsuwar kama aiki sabon Shugaban Kungiyar Tagwayen Engineer Hassan Ahmad makeri ya Wanda yayi Magana a madadin Sauran Shugabannin ya bada tabbacin zasu yi aiki tukuru tare da bujiro da Sabbin dabarun da zasu ciyar da Kungiyar gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...