Yanzu-Yanzu: Ganduje ya je yiwa Kwankwaso ta’aziyyar kaninsa

Date:

Daga Zara Jamil Isa

Gwamanan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci tawagar Gwamnatin Jihar Kano zuwa Garin Kwankwaso dake Karamar Hukumar Madobi don yin ta’aziyyar Kanin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso Kwamaret Inuwa Musa Kwankwaso.
Kadaura24 ta rawaito Idan ba’a mantaba inuwa Kwankwaso Wanda yake shakikin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya rasu ne a Jiya talata ,Inda akai Masa sutura a jiyan kamar yadda addinin Musulci yayi tanadi.
Yayin ta’aziyyar Gwamna Ganduje ya yiwa mamacin addu’a da fatan samun rahamar Ubangiji tare da Allah zai baiwa iyalai da yan uwan Marigayin Hakurin jure rashin.
Hakimin Madobi Makaman Karewa Alhaji Musa Sale Musa ne ya tarbi tawagar Gwamnan tare da godewa Gwamnan bisa ziyarar ta’aziyyar Dan uwansu da yaje musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...