Yanzu-Yanzu: Ganduje ya je yiwa Kwankwaso ta’aziyyar kaninsa

Date:

Daga Zara Jamil Isa

Gwamanan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci tawagar Gwamnatin Jihar Kano zuwa Garin Kwankwaso dake Karamar Hukumar Madobi don yin ta’aziyyar Kanin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso Kwamaret Inuwa Musa Kwankwaso.
Kadaura24 ta rawaito Idan ba’a mantaba inuwa Kwankwaso Wanda yake shakikin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya rasu ne a Jiya talata ,Inda akai Masa sutura a jiyan kamar yadda addinin Musulci yayi tanadi.
Yayin ta’aziyyar Gwamna Ganduje ya yiwa mamacin addu’a da fatan samun rahamar Ubangiji tare da Allah zai baiwa iyalai da yan uwan Marigayin Hakurin jure rashin.
Hakimin Madobi Makaman Karewa Alhaji Musa Sale Musa ne ya tarbi tawagar Gwamnan tare da godewa Gwamnan bisa ziyarar ta’aziyyar Dan uwansu da yaje musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...