Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

Date:

 

Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar da shirin kai farmaki a Nijeriya bayan umarnin tsohon shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, bisa zargin kisan Kiristoci a arewacin ƙasar kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

Rahoton ya nuna an tsara matakai uku wato mai nauyi, matsakaici da mai sauƙi domin bai wa gwamnati damar zabar irin martanin da ya dace ta ɗauka.

InShot 20250309 102512486

Shirin mai nauyi ya haɗa da tura jiragen yaƙi zuwa tekun Guinea don kai hare-hare a Arewacin Nijeriya, yayin da matsakaicin mataki zai dogara da jirage marasa matuka wajen kai farmaki kan sansanonin ’yan ta’adda.

Matakin na uku mai sauƙi kuma zai kasance haɗin gwiwa da sojojin Nijeriya domin yakar Boko Haram da sauran ƙungiyoyin ta’addanci, tare da kare fararen hula a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...

Barazanar Amuruka: Tinubu ya bukaci yan Nigeria su kwantar da hankulansu

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga...