Gwamnatin Kano ta sauyawa makarantar mata ta Mai Kwatashi matsugunni

Date:

Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano ta ɗauke Karantar Sakandare ta Mata ta Mai Kwatashi daga titin France Road, Sabongari zuwa unguwar Kaura Goje a karamar hukumar Nassarawa.

Freedom Radio ta rawaito cewa Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ne ya bada umarnin sakewa makarantar matsuguni biyo bayan koken ƴan unguwar Kaura Goje da kewayenta akan zargin yadda ake wa ɗaliban makarantar kwace da sauran su.

Tuni dai kungiyar cigaban unguwannin Kaura Goje, Gwagwarwa, Gawuna, Riga, da Gamar Fulani ta mika sakon godiya ga Gwamna Yusuf bisa cika alƙawarin sauyawa makarantar.

Mazauna unguwannin sun nuna farin ciki yadda aka kai makarantar kusa da su, musamman ma ganin cewa ta mata ce, inda su ka nuna cewa hakan zai kara habaka ilimin mata a yankin nasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Maikwatashi: Tsohon kwamishinan Ilimi ya rubutawa gwamnan Kano budaddiyar Wasika

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Alhaji Muhammad Sanusi...

Sule Lamido, Ya Yi Barazanar Maka Shugabannin PDP a Kotu

  Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana...

Tsofaffin Kansiloli Sun Yi Saukar Alƙur’ani da Addu’a na Musamman ga Gwamna Abba

  Ƙungiyar tsofaffin kansiloli na jihar Kano ta gudanar da...

Hisbah ta kama mutane 25 bisa zargin shirya auren jinsi a Kano

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama akalla mutane...