An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Date:

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta da tsakanin jama’a ya bayyana cewa an dauke fitaccen malamin addini, Shaikh Abduljabbar Nasiru Kabara, daga gidan yarin Kurmawa da ke Kano zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

Wata majiyar kusa da iyalan malamin ta shaida wa Kadaura24 cewa, daga baya suka ji rade-radin cewa an kai shi gidan yarin Kuje da ke Abuja, lamarin da ya tayar da hankula a tsakanin mabiyansa da ‘yan uwa.

A wata sanarwa da Askia Nasiru Kabara ya fitar a madadin iyalan Shaikh Abduljabbar, ya ce suna zargin akwai manufar siyasa ko wata bakar manufa a bayan daukar malamin daga Kurmawa zuwa wani wuri daban, musamman a wannan lokaci da ake samun sabbin jita-jita kan batun da ya shafi Shaikh ɗin.

“Mun sani hukumar kula da gidajen yari ta kasa tana da ikon mayar da fursuna duk inda ta ga dama, amma abin mamaki shi ne me ya sa sai yanzu aka dauke shi bayan shekaru hudu da yake a Kurmawa?” in ji Askia.

Ya kara da cewa, tun bayan barkewar maganar Lawan Triumph, an fara yada jita-jitar cewa za a saki Shaikh Abduljabbar, wanda hakan ya jawo cece-kuce daga bangaren kungiyar Izala.

Iyalan Shaikh din sun bayyana damuwarsu cewa yanzu da aka ce an mayar da shi Abuja, ba su da tabbacin yadda ake kula da shi, musamman wajen abinci da lafiya, domin kafin yanzu suna kai masa abinci daga gida.

A karshe, iyalan sun bukaci manyan jami’an gwamnati da hukumomi su sanya ido a cikin lamarin, ciki har da:

1. Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

2. Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima

3. Mai ba shugaban kasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu

4. Sufeton ‘yan sanda na kasa (IGP)

5. Daraktan DSS

6. Gwamnatin jihar Kano

7. Da kungiyoyin kare hakkin dan adam

“Abin da ya faru da Shaikh Abduljabbar ya zama abin damuwa da ya shafi tsaro da adalci a kasa baki daya. Bai kamata wasu kalilan su yi wasa da rayuwar mutum ba,” in ji sanarwar.

Iyalan sun roki gwamnati da hukumomin tsaro da su binciki lamarin da gaggawa domin tabbatar da cewa ba a tauye masa hakkinsa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...

Kananan Hukumomin Tarauni Rogo da Doguwa sun zamo koma baya wajen yin rijistar Masu zabe a Kano

Rahotanni sun nuna cewa ya zuwa yanzu kananan hukumomin...