Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Date:

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya Lokacin Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Na Gwamnoni Zuwa Nuwamba, 2026

An gabatar da Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe ta 2025 (Electoral Act Amendment Bill 2025) a yayin zaman sauraron ra’ayoyin jama’a da aka gudanar a Abuja a ranar Litinin, wanda Kwamitocin Majalisar Dattawa da na Majalisar Wakilai kan Harkokin Zaɓe suka shirya tare.

A cikin kudirin, majalisar ta ba da shawarar a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na gwamnonin jihohi a watan Nuwamba, 2026, wato watanni shida kafin lokacin da ake gudanar da irin wannan zaɓe a da.

Kudirin ya tanadi cewa, “Zaɓen ofishin shugaban ƙasa da na gwamnan jiha dole ne a gudanar da shi ba fiye da kwanaki 185 kafin karewar wa’adin mai rike da mukamin a yanzu.”

Wannan sabon tsarin zai sa zaɓukan gaba na ƙasa da jihohi su gudana a Nuwamba, shekarar 2026.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...

Kananan Hukumomin Tarauni Rogo da Doguwa sun zamo koma baya wajen yin rijistar Masu zabe a Kano

Rahotanni sun nuna cewa ya zuwa yanzu kananan hukumomin...

Taron Zuba Jari na Bauchi: Sabuwar Damar Bunƙasar Tattalin Arziki – Daga Lawal Muazu Bauchi

  Ga dukkan alamu, Jihar Bauchi na fitowa a hankali...