Nasarar da Ɗaliban Kano suka Samu a NECO Kokari ne na Gwamnatin Ganduje – Sanusi Kiru

Date:

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi Kiru, ya taya ɗaliban Kano murna bisa nasarar da suka samu a sakamakon jarrabawar kammala makaratun Sakandire ta NECO a Wannan Shekarar ta 2025, inda jihar ta zama ta farko a fannin Turanci da Lissafi.

Sanusi Kiru ya bayyana cewa wannan gagarumar nasara ba za a iya ta’allakata ga tasirin sauye-sauyen da gwamnatin Kano mai ci ba, sai dai alama ce dake nuna irin ingancceen fandisho da jarin da tsohon Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya zuba a bangaren Ilimi lokacin mulkinsa tun daga shekarar 2015 zuwa 2023.

Kiru ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

A cewarsa, ingantaccen shirin da aka aiwatar a wancan lokaci wajen inganta makarantu, horas da malamai da kuma samar da kayan aiki shi ya gina tubalin da ɗaliban suka dogara da shi wajen cimma wannan matsayi.

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Kiru ya jaddada cewa ba adalci ba ne a jingina nasarar da aka samu kacokan ga gwamnatin mai ci a yanzu ba tare da tuna irin rawar da aka taka a baya ba. Ya ce irin waɗannan sakamakon manya ne daga tsare-tsare masu dogon zango da kuma jajircewar gwamnatin Ganduje wajen bunƙasa ilimi a Kano.

FB IMG 1753738820016
Talla

Ya kuma yaba wa ɗaliban, malamai, iyaye da dukkan masu ruwa da tsaki da suka bada gudummawarsu wajen ganin wannan nasara ta tabbata.

A cewarsa, ” mun kira ga gwamnati Mai ci da ta ƙara dagewa domin ci gaba da inganta harkar ilimi a jihar, domin amfanin al’umma nan gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Amfani da al’ada a cikin fina-finan kannywood ne ya hana masa’antar ci gaba – Khadija Osi

Jaruma a masana'antar Kannywood Khadija Muhammad wacce aka fi...

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...

Kungiyar Karamci United Family ta Karrama Shugaban gidan Radiyon Pyramid Saboda Taimakawa Al’umma

Shugaban gidan Radio tarayya Pyramid FM Dr. Garba Ubale...