Gwamnatin Jihar Sokoto ta musanta Yunkurin Kashe Gwamna Tambuwal

Date:

Gwamnatin Jihar Sokoto mai fama da hare-haren ‘yan binidga a arewacin Najeriya ta musanta cewa an jikkata Gwamna Aminu Waziri Tambuwal da aka ce an kai wa tawagarsa a yankin Sabon Birni.

Wata sanarwa da matamakin gwamnan kan kafafen yaɗa labarai Muhammad Bello ya fitar ta ce duk da cewa gaskiya ne gwamnan da tawagarsa sun kai ziyara Sabon Birni ranar Juma’a amma “lafiya ƙalau”.

Rashin tsaron:Buhari ya tura Shugabanin Hukumomin tsaro jihohin Katsina da Sokoto

Wasu rahotanni da Daily Trust ta tattara sun ce ‘yan fashin daji sun sake kai hari a yankin ne inda suka kashe mutum uku tare da jikkata wasu da dama kwana biyu bayan sun ƙona mutum kusan 30 a cikin motar bas.

Sanarwar ta tabbatar da cewa Gwamna Tambuwal ya je Sabon Birni ne domin jajanta wa mazauna yankin kan harin da aka kai wa fasinjojin kafin sake kai wani harin a ranar Juma’a.

Labarin da ake yaɗawa (na raunata gwamna) ba gaskiya ba ne, wabda wata kafar labarai ta “Critical Times.” ke yaɗawa,” a cewar sanarwar.

Harin wanda shaidu suka faɗa wa BBC Hausa cewa ya faru ne da safiyar Litinin ya harzuƙa ‘yan Najeriya, har ma suka dinga sukar Shugaba Buhari kan tafiya taron ƙaddamar da littafi a Jihar Legas yayin da lamarin ke faruwa.

2 COMMENTS

  1. קמגרה תשדרג לכם את חיי המין ותאפשר לכם הנאה מרבית מהאקט. לטבע פלז’ר שלל פתרונות טבעיים נוספים שישדרגו לכם את חדר המיטות. קמגרה תשדרג לכם את חיי המין ותאפשר לכם הנאה מרבית מהאקט. לטבע פלז’ר שלל פתרונות טבעיים נוספים שישדרגו לכם את חדר המיטות. מכוני ליווי

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...