Tinubu ya bijiro da harajin da zai sa farashin man fetur ya karu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙaddamar da sabon harajin shigo da kaya na kashi 15 cikin 100 kan dukkan man fetur da dizil din da aka shigo da shi zuwa Najeriya..

An bayyana cewa wannan mataki na gwamnati na da nufin kare matatun man fetur na cikin gida da kuma daidaita kasuwar man fetur ta ƙasa, sai dai ana hasashen zai iya haifar da ƙarin farashin mai a matakin farko.

Wannan umarni na Shugaban Ƙasa na ƙunshe ne a cikin wata wasika da aka aika ta zuwa ga hukumar tara haraji ta Ƙasa da hukumar kula da albarkatun man fetur ta kasa domin aiwatar da sabon tsarin nan take.

FB IMG 1753738820016
Talla

Wasikar, wacce mai taimakawa Shugaban Ƙasa, Damilotun Aderemi, ya sanyawa hannu , ta nuna cewa an amince da shirin ne bayan shawarar da shugaban hukumar haraji Zacch Adedeji, ya gabatar.

A cikin shawarar da ya mikawa shugaban ƙasa, Adedeji ya bayyana cewa harajin zai shafi kimar kaya,da inshora da kuɗin jigilar na dukkan mai da ake shigo da shi, domin daidaita farashin shigo da mai da na cikin gida.

Gwamnatin Kano Ta Karyata Rahoton Cibiyar Wale Soyinka Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida

Ya ƙara da cewa wannan mataki wani ɓangare ne na ci gaban sauye- sauyen gwamnati domin ƙarfafa tace mai a cikin gida, da tabbatar da

daidaiton farashi, da kuma ƙarfafa tattalin arzikin mai bisa kuɗin naira, bisa tsarin sabunta fata na gwamnatin Tinubu don tabbatar da tsaron makamashi da dorewar tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...