Rashin tsaron:Buhari ya tura Shugabanin Hukumomin tsaro jihohin Katsina da Sokoto

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya aika da tawaga ta musamman zuwa Sokoto da Katsina sakamakon yadda ƴan bindiga ke ci gaba da kai hare-hare a yankunan jihohin.

Mai magana da yawun shugaban Najeriyar Malam Garba Shehu ya sanar da hakan inda ya ce shugaban yana jiran rahoto cikin gaggawa da kuma shawarwari kan matakin da ya kamata a ɗauka domin magance matsalolin da jihohin ke fuskanta.

Cikin waɗanda Buharin ya tura akwai babban mai ba shi shawara kan harkokin tsaro Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya da Babban Sufeton ƴan sandan Najeriya Usman Alkali Baba da daraktan hukumar tsaro ta farin kaya Yusuf Magaji Bichi da daraktan hukumar tattara bayanan sirri ta Najeriya Yusuf Magaji Bichi da kuma shugaban tsaro na rundunar sojin Najeriya Manjo Janar Samuel Adebayo.

Wannan matakin dai na zuwa ne jim kaɗan bayan yan ƙasar da dama sun nuna ɓacin ransu kan kasashe-kashen da ake ƙara samu da garkuwa da mutane a ƙasar.

Ko a yau ma sai da wasu yan ƙasar suka fita zanga-zanga a wasu sassa na Najeriya har da Abuja babban birnin ƙasar.

1 COMMENT

  1. קמגרה תשדרג לכם את חיי המין ותאפשר לכם הנאה מרבית מהאקט. לטבע פלז’ר שלל פתרונות טבעיים נוספים שישדרגו לכם את חדר המיטות. קמגרה תשדרג לכם את חיי המין ותאפשר לכם הנאה מרבית מהאקט. לטבע פלז’ר שלל פתרונות טבעיים נוספים שישדרגו לכם את חדר המיטות. מכוני ליווי

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...