A Hukuma ce INEC ta bayyana sakamakon zabukan cike gurbi da aka yi a kano

Date:

Hukumar zabe mai zamanta ta Kasa ta bayyana Dan takarar Jam’iyyar NNPP Ali Lawan Alhassan a matsayin wanda ya lashe zaben cike gurbi na dan majalisar Jiha na kananan hukumomin Bagwai da Shanono da kuri’u 16,198.
yayin da dantakarar APC ya samu kuri’u 5,347.

Baturen zaɓen Farfesa Hassan Adamu Shitu ne ya sanar da sakamakon da misalin ƙarfe 12:36am.

FB IMG 1753738820016
Talla

Haka zalika hukumar zaben ta bayyana Dan takarar Jam’iyyar APC Garba Yau Gwarmai a matsayin wanda ya lashe zaben Dan Majalisar jiha mai wakiltar kananan hukumomin Ghari da Tsanyawa a Majalisar dokokin jihar Kano .

Baturen zaɓen yankin, Farfesa Muhammad Waziri, ne ya sanar da sakamakon zaben da ƙarfe 6:10 na safiyar wannan Lahadi.

Farfesa Waziri ya ce jam’iyyar APC ta samu kuri’u 31,472, yayin da NNPP ta sami kuri’u 27,931.

Adan haka ya ce Garba Ya’u Gwarmai, na jam’iyyar APC ne ya lashe zaɓen cike gurbin na mazaɓar Ghari da Tsanyawa a majalisar dokokin jihar Kano, da aka gudanar a jiya Asabar .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Adam A Zango ya sake Aurar Jarumar Kannywood

Fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finan Hausa, Kannywood, Adam A....

NNPP ta yi watsi da sakamakon Zaben Ghari da Tsanyawa a Kano

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta ƙi amincewa da...

Kwankwaso ya yi tsokaci game da zaben cike gurbi da akai a Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana...

PDP ta yi watsi da zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono dake Kano

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kano Arewa maso Yammacin Najeriya...