Za a ci tarar Naira N100,000 kan duk wanda ya sare bishiya a Abuja

Date:

Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja ta ce daga yanzu duk wanda aka samu da laifin sare bishiya zai biya tarar N100,000.

Hukumar ta bayyana haka ne a sakon da ta wallafa a shafinta na Twitter ranar Litinin.

Sanarwar ta ambato Daraktar kula da wuraren shakatawa, Mrs Riskatu Abdulazeez, tana kara da cewa “haramun ne sare bishiyoyin da aka dasa a cikin gidajen jama’a ba tare da neman izinin gwamnati ba.”

A cewarta sare bishiyoyin na ta’azzara matsalolin da ke da dangantaka da sauyin yanayi don haka ba za su bari mazauna birnin su ci gaba da sare bishiyoyi ba tare da la’akari da illar yin hakan ba.

“Duk wanda ya sare bishiya ba bisa ka’ida ba zai biya tarar N100,000 kuma za a tilasta masa dasa sabbin bishiyoyi biyu domin maye gurbin wacce ya sare.” in ji Mrs Riskatu

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah : Kansilan Lajawa ya raba Naira dubu 500 ga al’ummar mazabarsa

Daga Nura Adam   Kansilan mazabar Lajawa a karamar hukumar Wudil...

Da dumi-dumi: Kotu ta aike da Matashin dake shigar mata a Tiktok da film gidan gyari

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Hukumar tace fina-finai da Dab'i...

Rabon Jakai: Faizu Alfindiki ya aikawa Sanusi Bature budaddiyar wasika

Zuwa ga: DG. Sunusi Bature Dawakin Tofa Daraktan Yada Labarai, Gwamnatin...

Dama ba mu yi shirin yin hawan babbar Sallah ba – Sarki Aminu Ado Bayero ya fadi dalili

Daga Isa Ahmad Getso   Sarkin Kano na 15 Aminu Ado...