An Umarci Limaman Masallatan Juma’a a Kano su gudanar da Hudubar gobe Juma’a akan Zaman Lafiya

Date:

Daga Usman Hamza Usman
An umarci daukacin limaman Masallatan juma’a a jihar kano da su  Shiryya Hudubar gobe juma’a akan Muhimmancin  Zaman Lafiya a tsakanin Al’ummah.
Kadaura24 ta rawaito Shugaban Majalisar Limaman Masallatan juma’a na jihar kano Sheikh Muhammad Nasir Adam ne ya bayyana hakan yayin Ganawarsa da manema labarai .
Sheikh Muhammad Nasir yace zaman lafiya shi ne Kashin bayan cigaban kowace Al’ummah, a don Haka ya baiwa Limaman Jihar Kano Umarnin yin huduba akan hakan.
” Addinin Musulci ya baiwa Zaman Lafiya muhimmanci sosai ,shi yasa ake Kiran addinin a Matsayin addinin Zaman Lafiya, don haka muka bada Umarnin ga limamai dau yi Amfani da damar da Allah ya basu Wajen fadakar da al’umma muhimmancin Zaman Lafiya” inji Sheikh Nasir Adam
Sheikh Nasir Adam  Wanda shi ne Babban Limamin masallacin Juma’a na Sheikh Ahmadu Tijjani dake Kofar mata kara da cewa suma limaman Masallatan Unguwanni na Khamsussalawatu dake fadin jihar nan Su cigaba da Addu’o’in Samun Zaman lafiya a jihar kano da kasa baki daya.
Shehun Malamin yayi fatan Samun sauki ga sauran jahohi da  kasashen da iftila’in  rikici ya addabesu.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...

Al’ummar Kano ku baiwa AA Zaura hadin Kai domin ya kawo karshen fadan Daba – Baba Yawale

Daga Halima Umar Dogo   Babban Hadimin AA Zaura Alhaji Baba...