JOHESU ta Zabi Sabon Shugaba a Kano

Date:

Daga Kabir Muhd Getso

 

Hadaddiyar Kungiyar Ma’aikatan Lafiya ta kasa Reshen Jihar Kano JOHESU ta zabi Sabon Shugabanta a Kano.

 

Com Ibrahim Muhammad Maikarfi Shi ne ya lashe zaben da aka gudanar jiya a sakatariyar kungiyar dake cikin Birnin Kano.

 

Comrade Makarfi kafin zabarsa shi ne Shugaban kungiyar ma’aikatan jinya da Unguwar zoma na jihar kano Wato Nursing and Midwifery Association Of Nigeria.

 

Da yake Zantawa da wakilin Kadaura24 Maikarfi ya Godewa Allah bisa wannan dama da ‘ya’yan kungiyar suka bashi na jagorantarsu, Sannan ya sha Alwashin cigaba da jajircewa wajen ciyar da kungiyar gaba.

 

Ya Kuma bukaci hadin Kan ‘ya’yan Kungiyar don su bashi hadin Kan da ya kamata domin ciyar da Kungiyar gaba.

 

Kazalika yayi kira da wadanda suka nemi wannan matsayi basu samu ba da su cigaba da bada tasu gudummuwar wajen ciyar da kungiyar gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...