JOHESU ta Zabi Sabon Shugaba a Kano

Date:

Daga Kabir Muhd Getso

 

Hadaddiyar Kungiyar Ma’aikatan Lafiya ta kasa Reshen Jihar Kano JOHESU ta zabi Sabon Shugabanta a Kano.

 

Com Ibrahim Muhammad Maikarfi Shi ne ya lashe zaben da aka gudanar jiya a sakatariyar kungiyar dake cikin Birnin Kano.

 

Comrade Makarfi kafin zabarsa shi ne Shugaban kungiyar ma’aikatan jinya da Unguwar zoma na jihar kano Wato Nursing and Midwifery Association Of Nigeria.

 

Da yake Zantawa da wakilin Kadaura24 Maikarfi ya Godewa Allah bisa wannan dama da ‘ya’yan kungiyar suka bashi na jagorantarsu, Sannan ya sha Alwashin cigaba da jajircewa wajen ciyar da kungiyar gaba.

 

Ya Kuma bukaci hadin Kan ‘ya’yan Kungiyar don su bashi hadin Kan da ya kamata domin ciyar da Kungiyar gaba.

 

Kazalika yayi kira da wadanda suka nemi wannan matsayi basu samu ba da su cigaba da bada tasu gudummuwar wajen ciyar da kungiyar gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...