Daga Maryam Abubakar Nice
Hatsarin kwale-kwalen daya faru a Bagwai, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 20, yayin da ake ci gaba da aikin ceto Wasu da hatsarin ya rutsa dasu Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya bayyana hatsarin a matsayin Iftila’in daya shafi duk al’ummar Jihar Kano.
Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne Cikin Wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran as Malam Abba Anwar ya Sanyawa Hannu Kuma ya aikowa Kadaura24.
“Mun samu labarin cewa jirgin ya taso ne daga Hayin Badau zuwa Bagwai a kan hanyarsu ta zuwa halartar bikin Mauludi, yayin da jirgin ke dauke da mutane kusan 50 dauke da wasu kaya, wanda ya kife saboda da yawa Nauyin da aka yi Masa, Kuma yawancin Mutanen ciki daliban Islamiyya ne.” A cewar gwamnan.
“A yayin da muke addu’ar Allah ya gafartawa wadanda suka rasu ya kuma baiwa wadanda suka jikkata lafiya cikin gaggawa, ina kira ga matuka irin Wadancan jiragen ruwa da su dai daukar Mutanen da suka wuce kima don gudun salwantar da rayukan al’umma.Ya kamata su sani cewa har yanzu za su iya samun riba ba tare da yin lodin da ya wuce kima ba a Cikin kwale-kwalensu ba,” in ji Ganduje.
“Ya zuwa yanzu, bisa ga bayanin da muka samu, domin a safiyar yau Laraba an samu mutuwar mutane 20, yayin da Mutane 7 ke kwance a asibiti, an kuma gano wasu 8 a safiyar yau kuma ana ci gaba da aikin ceton wasu, muna jinjina wa jajircewa da kishin kasa. na kungiyoyin bada agaji” in ji shi.
Idan ba’a mantaba taba Shekaru sama da goma da suka gabata an taba Samun irin Wannan hatsarin kwale-kwalen Wanda shi ma ya yi sanadiyyar mutuwar Mutane da dama.