Minjibir Journalist Forum na mika sakon ta’aziyya da alhini ga daukacin al’ummar karamar hukumar Minjibir bisa rashin wasu jiga-jigan al’umma da suka rasu a ‘yan kwanakin nan.
Wadanda suka rasu sun hada da:
Marigayi Engr. Salisu Abdulwahab (Galadiman Tsakuwa) – Fitaccen dan kasa mai kishin al’ummarsa.

Marigayiya Nasiba Sabo (Matar Isma’il Bello) – Uwar gida nagari da aka san ta da kyawawan halaye.
Dr. Bashir Aliyu Umar ya Sami Babban Mukami a Nigeria
Marigayi Alhaji Bala Zabainawa – Tsohon Sakataren Mulki na karamar hukumar Minjibir wanda ya bayar da gudunmawa wajen cigaban al’umma.
Marigayi Hon. Malam Saleh Ado Minjibir – Tsohon shugaban majalisar matasa, tsohon babban sakatare a gwamnatin jihar Kano kuma tsohon shugaban karamar hukumar Minjibir.
Marigayi Malam Sani Hamza Tsoho – Ma’aikaci a makarantar sakandaren ‘yan mata ta gwamnatin tarayya dake Minjibir, wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen ilimantar da mata.
Muna addu’ar Allah ya gafarta musu, ya jikansu da rahama, ya basu Aljannah Firdausi. Haka kuma muna rokon Allah ya baiwa iyalansu, ‘yan uwa da daukacin al’ummar Minjibir hakurin jure wannan babban rashi.
Mai Sanarwa:
Hussaini Kabir Minjibir
Domin Minjibir Journalist Forum