Tinubu ya sake ƙaddamar da aiki titin Abuja zuwa Kaduna

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gina babbar hanya daga Abuja zuwa Abuja zuwa Kaduna zuwa Zaria zuwa Kano.

Uba Sani gwamnan Kaduna ne ya wakilci Tinubu a wajen taron.

FB IMG 1744283415267
Talla

A wajen taron kaddamar da aikin, wanda ya gudana a Jere a karamar hukumar Kagarko a jiya Lahadi, Sani ya ce titin babbar hanya ce mai matukar muhimmanci ga rayuwar zamantakewa da tattalin arzikin Arewacin Najeriya.

Gwamnatin Kano za ta inganta walwala ma’aikatan dake kula da harkokin kudi – Babbar Akanta

Ya bayyana hanyar a matsayin babbar hanyar da ta haɗa babban birnin tarayya Abuja zuwa sama da jahohi 12 a shiyyar arewa ta tsakiya, arewa maso yamma da arewa maso gabas.

Daily Nigerian Hausa ta tuna cewa watannin baya Ministan Aiyuka, David Umahi, yayin ƙaddamar da aikin wani sashe na titin ya ce za a kammala aikin titin mai tsawon kilomita 700, ya ce za a kammala shi a cikin watanni 14.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...