Sanata Kawu Sumaila ya Raba Babura 150 ga wasu yan Kano ta Kudu

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Sanata Suleiman Abdurrahman Kawu Sumaila, ya raba babura 150 a fadin kananan hukumomi 16 dake amazabar sanatan Kano ta Kudu a wani yukuri na tallafawa wadanda suka taimakawa tafiyar gidan Siyasarsa.

Tallafin ya shafi mutane da dama, da suka hada da magoya bayansa guda uku-uku na kananan hukumomi 16, da mabiya addinin Musulunci dana Kirista, da kungiyar Waraka Media, da Waraka Band, jami’an tsaro na Waraka, da sauran mabiya da dama daga sassan jihar Kano.

InShot 20250309 102403344
Talla

Da yake jawabi yayin bikin rabon tallafin, Sanata Kawu Sumaila, ya bayyana cewa ya samar da baburan ne domin tallafawa wadanda suka yi dawainiya da takararsa har ya sami nasara.

“Rabon wadannan babura kari ne kan godiya bisa yadda kuka jajirce akan takarar Kawu Sumaila har ya sami don haka na ga dacewar kuma na gode muku ko kwa kara kwarin gwiwa”.

Rundunar Yansanda ta gayyaci Sarki Sanusi II

A wata sanarwa da mai taimakawa sanatan kan harkokin yada labarai Abbas Adam Abbas ya fitar, ya ce Kawu ya kuma yi alkawarin cigaba da tallafawa wadanda suka dafa masa tare kuma da gudanar da aiyukan da kowanne dan Kano ta Kudu zai amfana.

Wannan dai shi ne karo na shida da Sanata Kawu Sumaila ke tallafawa mutanensa tun bayan hawansa mulki a ranar 13 ga watan Yunin 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...