Rundunar Yansanda ta gayyaci Sarki Sanusi II

Date:

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta gayyaci Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, domin amsa tambayoyi kan wani lamari da ya faru a yayin bikin Sallah karama a Kano.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta ruwaito cewa a ranar Lahadi, 30 ga Maris, 2025, rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wani Usman Sagiru, mai shekaru 20, dan unguwar Sharifai, bisa zargin kisan wani dan Vigillante dake cikin tawagar Sarki Sanusi II bayan sallar idi.

Hakazalika rundunar ta fara gudanar da bincike kan lamarin wanda hakan ya sa ya gayyaci Shamakin Kano, Alhaji Wada Isyaku domin ya amsa wasu masa tambayoyi.

InShot 20250309 102403344
Talla

 

A cewar wata wasika a hukumance da Kadaura24 ta gani mai dauke da kwanan watan Afrilu 4, 2025, kuma mai dauke da sa hannun CP Olajide Rufus Ibitoye, kwamishinan ‘yan sanda (Ayyuka), an gayyaci sarki Sanusi ne bisa umarnin babban sufeton ‘yan sandan Nigeria.

Wasikar ta bukaci Sarkin da ya kai kansa hedikwatar rundunar da ke Abuja sashin tattara bayanan sirri a ranar Talata, 8 ga Afrilu, 2025, da karfe 10:00 na safe.

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da ranakun komawa makaranta

Hukumomin tsaro sun bayyana hana hawan sallah, saboda yiwuwar samun tashin hankali.

An dai zargi Sarki Muhammadu Sanusi da yin hawa ranar Sallah da hawan daushe da kuma Hawan Nasarawa inda ya kai ziyara ga gwamnan jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...